ArewaJazeera
  • About
  • Blog
  • Contact
  • FAQ
  • Home
Monday, March 2, 2026
  • Login
No Result
View All Result
No Result
View All Result
ArewaJazeera
No Result
View All Result
Home Hausa News

Mijina Ya Zabi Sabuwar Amarya, Ya Barni Cike Da Damuwa

Malamar Aji by Malamar Aji
November 11, 2025
in Hausa News
0

A wata hira da jaridar Arewa Jazeera ta yi da wata mata, ta bayyana yadda rayuwarta ta canza bayan mijinta ya kara aure.

Ta fara da cewa:
“Bayan mijina ya auri budurwa, ya tuntube ni inyi yi hakuri zai shafe kwanaki bakwai tare da ita kafin ya dawo dakina kamar yadda aka saba. Amma sai ya dauki sati biyu ba tare da ya dawo ba, daga bisani lokacin ya zo ya roke ni in kara masa sati biyu tare da sabuwa. Duk da raina ya baci, sai na daure na amince.”

“Da suka cika sati hudu tare, na fara period a ranar zan karbi girki. Mijina ya kuma roke ni in bari ya kwana da sabuwar amaryarsa saboda halin da nake ciki, na amince. Bayan kwana biyar da zan samu lafiya, sai hutun aikin mijina ya kare, zai koma Abuja. Ya zo ya ajiye takardu a gabansa yana son mu zabi. Ni na zabi ‘zaman gida’, ita kuma sabuwar amarya ta zabi ‘tafiya Abuja’. Mijina ya yi dariya, muka yi sallama.”

Ta ci gaba:
“Bayan yaje Abuja ya dawo hutun sati biyu kamar yadda ya saba sai ya barta a can, na lura da saƙonni na soyayya daga sabuwar amarya a wayar mijina; tana roƙonsa kada ya dade ba tare da ya koma can ba. Wannan abu ya dagula min rai, amma na daure. Bayan wani lokaci mijina ya shigo cikin gaggawa, wai an masa kira daga aiki. Na masa fatan alkhairi. Kafin ya fita falo, na fadi na suma – aka kai ni asibiti, har kwana daya muka dawo gida.”

“Tun daga wannan lokaci sabuwar amarya tana zuwa da kiransa tana jin halin da nake ciki. Har abokinsa ya kawo ta gidanmu, ta kwana biyu. Yanzu kuma, mijina zai koma Abuja, na shaida masa ko ta zauna sai ya hada mu duka mu tafi, domin na gaji da halin rashin tabbas.”

Ta kammala hirarta da kalmomin hakuri da tausayi, tana fatan samun kwanciyar hankali da zaman lafiya.

Related Posts

Kalla Bidiyo: ‘Yan Matan Da ‘Yan Bindiga   Suka Sace Tsakanin Sokoto da Zamfara
Hausa News

Kalla Bidiyo: ‘Yan Matan Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Tsakanin Sokoto da Zamfara

February 24, 2026
Maryam Yahaya Ta Jawo Cece-Kuce a TikTok Bayan Tayi Live Dauke da Jariri A Hannu
Hausa News

Maryam Yahaya Ta Jawo Cece-Kuce a TikTok Bayan Tayi Live Dauke da Jariri A Hannu

February 23, 2026
Idan Kana Son Zama Mai Kuɗi, Dole Ka Sadaukar Da Waɗannan Abubuwa 10
Hausa News

Idan Kana Son Zama Mai Kuɗi, Dole Ka Sadaukar Da Waɗannan Abubuwa 10

February 21, 2026
Ana Zargin Maryam Yahaya da Amfani da Magungunan Ƙara Girman Jiki
Hausa News

Ana Zargin Maryam Yahaya da Amfani da Magungunan Ƙara Girman Jiki

February 17, 2026
Ango Ya Saki Amarya Saboda Rashin Nono — Darasi Ga Masu Shirin Aure
Hausa News

Ango Ya Saki Amarya Saboda Rashin Nono — Darasi Ga Masu Shirin Aure

February 17, 2026
“Nakan ji kunyar shiga mutane saboda manyan nonuwana”
Hausa News

Abubuwa 5 Da Namiji Zai Duba Kafin Ya Amince Wa Mace

February 16, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • About
  • Blog
  • Contact
  • FAQ
  • Home

© 2025 ArewaJazeera.com

No Result
View All Result
  • About
  • Blog
  • Contact
  • FAQ
  • Home

© 2025 ArewaJazeera.com

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In