Wata budurwa marar aure ta kwana a gidan wani saurayi mai shekaru 25 a ɗaki ɗaya, tsawon dare guda bayan ta bace hanya.
Ta bayyana masa cewa ita ɗaliba ce, kuma ta rasa hanyar komawa gida bayan malamarta sun tafi suka bar ta.
Saurayin ya tausaya mata, ya shigar da ita gidansa domin ta kwana har zuwa safiya.
Ya ba ta gadonsa, shi kuma ya kwanta a ƙasa, sannan ya raba ɗakin gida biyu da igiya domin tabbatar da mutunci.
A cikin dare, budurwar ta lura saurayin yana ƙona yatsunsa a kan wutar kyandiri ɗaya bayan ɗaya.
Ta tsorata ƙwarai, tana tunanin ko yana aikata wani abu na al’ajabi.
Babu wanda ya iya yin barci a daren.
Da safe, saurayin ya mayar da ita gidansu lafiya.
Washegari mahaifinta ya ziyarce shi, inda ya ga hannunsa a ɗaure da bandeji. Da ya tambaye shi dalili, saurayin ya ce:
“Shaidan ya yi ta jarrabata a zuciyata domin in aikata alfasha.
Duk lokacin da sha’awa ta taso, sai na ƙona yatsana da wuta domin in tuna azabar lahira, in tsare kaina daga zunubi.”
Darasi: Hakuri da tsoron Allah na iya kare mutum daga fadawa cikin kuskure, ko da jarraba ta yi tsanani.






